19 Yuni 2025 - 05:53
Source: ABNA24
Ministan Makamashin Isra'ila: Sake Gina Matatar Man Haifa Zai Bukaci Wata Guda

Ministan Makamashin gwamnatin Sahayoniya ya sanar da cewa sake gina matatar ta Haifa yana bukatar wata guda. 

Kamfanin dillancin labaran ƙasa da ƙasa na Ahlulbayt (AS) - ABNA - ya habarta cewa: Hukumar Kula da Makamashi ta Sahayoniya tace: "Cikakken sake gina matatar mai ta Haifa da sake kafa ayyukan tashar wutar lantarki na yau da kullun bayan harin makami mai linzami na Iran yanzu zai kai akalla wata guda.

Ministan Makamashi na Sahayoniya Eli Cohen matatar mai ta Haifa tana samar da Kashi 60% na iskar Gas da kashi 40 cikin 100 na man fetur ga Isra'ila, kuma wuri ne na babban kamfanin mai na gwamnatin sahyoniyawa. 

Isra'ila tun ranar Talata ta hana shigar yan jaridan ƙasa da ƙasa wajen domin yin aikinsu na watsa hotunan harin makamai masu linzami ga wannan matatar mai.

Your Comment

You are replying to: .
captcha